A cewar rahoton wakilin sashen ƙasa da ƙasa na Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, biyo bayan rasuwar babban malami kuma marja'i mai daraja, Hazrat Ayatullah Al-Uzma Sheikh Muhammad Ishayq Fayyadh, Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya fitar da saƙon ta'aziyya.
Ga fassarar saƙon kamar yadda yake:
Bismillahir Rahmanir Rahim
Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un
Muna miƙa ta'aziyyar rasuwar babban marja'in addini, Hazrat Ayatullah Al-Uzma Sheikh Ishaƙ Al-Fayyadh ga manyan marja'an addini, musamman ma na birnin Najaf Al-Ashraf, da daukacin al'ummar Musulmi na duniya. Muna rokon Allah Mai girma da gafarar zunubai da ya sanya shi a cikin faffadan aljannarSa madaidaciya, kuma ya daukaka darajar wannan malami na Ubangiji.
Ra'ayinka